*ANCUCI🤦🏼♀HIJJABI*
*TRUE LIFE STORY*
✏ _Written by_
*fayeeeeex m usman*
💦💦 *Talented writers forum* 💦💦
*had'in kanmu abin alfaharinmu🤝kungiya d'aya tamkar da dubu*
_domin samun littattafan mu shiga....
_To get access to talented novels check_
http://talentedwrittersnovel.blogspot.com/
❤💚💙 _masha allah masha allah masha allah ayau ina cikin_ *farin ciki marar musaltuwa sannu ISLAH TASI'U AYAU gaidake yau ranar farin cikin mune nahaufo mana Baby* _dakikai ubangiji ya allah yarayata ya d'aiyabata yasa_ *hafizace ameeeen...* 💙❤💚
*pg1⃣5⃣*
_aloqaci d'aya tasunkuyar da kanta tare da dafe qirjinta bugon da yake tana jiyo qararshi take taji qafafunta suna qoqarin gaza d'aukar da suke mata,kallo d'aya kaiwa Ummi kasan tsoro yagama kasheta jin kowa yai shiru kuma ita ake kallo yasa tai qarfin halin d'aga kanta ahankali idon tane ya sauke akan Ammi wacce ke tallabe da kuncinta hancinta da bakinta kuma jini_ _sai d'iga yake,Khdijat ma wadda ta miqe sai yanzu takai dubanta kan Ammin tasu dum! taji zuciyarta tayi naganin tabo ajikin mahaifiyarsu wanda iya rayuwa bata ta6a ganiba amma yau asanadin Ummi anzo hargida y'anci mutuncin iyayanta agabanta,kukane mai qarfi ya qwacema Khadijat tare daqarasa wajan Ammin tare suka isa da Ummi,wani mugun Kallo Ammi ta watsama Ummi wanda yasa taivaya,Kutti bala'i wacce ke tsaye da d'amararta tana watsama Ummi wani kallo so take mutum d'aya yai mata mgn acikinsu ta kama Ummi da_ dukan mutuwa,qara fashewa da _matsanancin kuka Khadijat tai asanda taga hawaye yagama wanke fuskar Ammi,d'ankwalin kanta tacire tanaqoqarin goge mata inda ya6aci dajini,ture hannunta Ammi tai tare da kawar da fiskarta gaba d'anyansu sunyi jigum,muguwar qarar da Ummi tasakine ya dawo da hankalinsu kanta,daman tsayuwar da Kuttin bala'i tai fakaitar idon su Abba take dan karsu hanata,dukan Ummi take takowanne 6angare,amma ba wanda ya tankamata,hankalin Hassina baqaramin tashi yaiba don ita atunaninta duk laifin da Ummi tai aebaikamata aga ana mata dukan mutuwa irin wannanba amma aeshiru,afakaice taleqa fuskar_ _Baba da kowa taga bamaishirin yin mgn, da gudu taje tana dukan D'ahare akan kafad'a wata bangaza Taiwa Hassina wanda yai sanadin fad'uwarta da 6as!batare da gajiyawa ba Hassina ta qara qoqarin miqe bokatan dasuke zuba ta nufa wata babbar roba ta gani d'aukarta tai tare da kanfato ruwa,Kuttin bala'i wacce ba_ _kunya ba tsoran allah tahaye kan y'ar mutane sai jibga take ba tausayi bare tausayawa,saiji tai anwatsa mata ruwa dagudu ta miqe akan Ummi wacce take motsa jikinta ahankali,da sauri Hassina taqarasa kan Ummi tana jijjigata wasu zafafan hawaye naratsowa takan kuncinta juyowa tai suka had'a ido hud'u da kuttin Bala'i,"baiwar allah ko mutuwa Hausawa suna cewa tana jin kunyar idon mahaifi bare ke y'ar adam wacce akewa laqabi da Musulma na tabbata ko arne zaiji kunyar_ _aekata abun da kikaye bare ke amma naga ko kad'an baki da muba to naji idan ramuwace kin ramawa y'arki ko?saiki fita kibarmana gidako inbaso kike ta mutuba.taqarashe tana mai fashewa da kuka ta6e baki Kuttin bala'i tai tana mai cewa cikin hucin bala'i,"aedaman duk wanda ya ta6oni baisan wacece niba to da Amina tagajeni Ummin banza mai ta'isa tai mata yarinya kad'anma kikagani wannan somun ta6ine.tana kaiwa qarshe tafice tana mai qara d'ura musu ashar,duk hayaniyar da ake su Imran naji kasan cewar katangace tsakaninsu ranshi baqaramin_ dad'i ya jiba kazalika ba qaramin _godewa Kuttin bala'i yaiba hakan yasa ya hana kowa na gidan fita tare da labartawa iyayanshi zagin da Ummi tamai agaban mahaifinta amma baice komaiba aeko tuni suka d'au zafi Malam Rabi'u ma yace gobe da sassafe zaije ya kar6i kud'inshi kuma ko gaisuws bazata qara shiga tsakaninsuba...
_
_kubiyoni_
✍🏼✍🏼✍🏼 *fayeeeeeeeex m usman*
Comments
Post a Comment