Skip to main content

Kece kaddarata

*KECE KADDARATA*
     
          *2017*

*Story and written by:*
*Halieymerh Ameen💕*

       *T.W.F*

       *Page 21 to 25*

  Bayan sun gama cin abinci suka koma parlour   suna hora ,Abdul dai tunda aka fara hirar baice uffan ba yana rike da carbi a hannunsa yana lazimi.Nazifa ce ta kalli Habib tace
"Yaya next week ma Inshaa Allah ya kamata na fara zuwa asibiti fa"
"Su autan Umma anzama Doctor ayya barka na dai" cewar Umma
"Wani asibiti kenan?"
"Eh Yaya medical centre zanje kuma tare da kai zamuje ko yayana" murmushi yayi
"To shikenan zamuje tare". Abdul dai mamakin surutun Nazifa yake bakinta baya iya shiru ga sakalci ina ma ace shima yanada kanwa nanda nan yaji zuciyarsa tayi masa zugi. Haka suka cigaba da hirarsu sai da lokacin sallar maghrib yayi kowa yatashi zuwa sallah.

Bayan kwana biyu Nazifa na kwance a cinyan Ummanta tana bata labarin makarantarsu, shiru tayi na dan kankanin lokaci sannan tace
"Umma dai baki bani labarin wayene wannan Yaya Abdul din ba har yanzu" kallonta Umma tayi kafun tace
"Meyasa kikeso ki sanine"  marairaice wa tayi
"Ayya Umma bansan mutum ba naganshi a gidanmu yana rayuwa a gani na ba laifi bane idan na tambaya ko"
"Ba laifi bane autan Umma".

Umma ta fara bata labarin haduwarsu da Abdul da duk wani abun da ta sani a kansa. Tausayin Abdul ne ya kama Nazifa taji ta matsu taji tarihinsa da kuma abunda ya kawoshi Katsina tunda alamu ya nuna shi ba dan garin bane.

Kullum Nazifa tana cikin jinjina al'amarin Abdul duk tabi ta damu haka kawai take so taga ta kyautata masa wataran idan taga yanda yake zama shiru har hawaye takeyi, koda yaushe tana cikin saqe saqe a zuciyarta tana tunananin yanda za'ayi ta san labarinshi ko zata daina wannan damuwan.
Umma ta lura da chanji tattare da ita gashi kullum se tayi mata zancen Abdul tun tana biye mata har ta daina sabida yanda taga abinnata yana wuce gona da iri ga yanda take shishige masa da son jansa da surutu sedai shidin dama ba mutum ne maison magana ba sedai yana amsa mata jifa jifa yana murmushi wanda yake kara mata kwarin guiwan son zama tare dashi, haka kawai sai Nazifa ta shiga kitchen tayi girki ta kai masa tana zaune yaci koda ya koshi yana iya kokarin sa yaci sabida yaga ta damu dashi bai kamata ya gwasale ta ba.

*(MASU KARATU WAI ME NAZIFA TAKE NUFI NE?🤔 IRIN WANNAN CUSA KAI HAKA🤣🤣🤣🤣🙊........MUJE ZUWA DA SANNU ZAMUJI MIYE NAZIFA TAKE NUFI DA ABDUL-ALI)*

 

   A kwana a tashi Abdul yana rage tunanin *KADDARAR SA*sedai kullum baya mancewa da mahaifiyarsa a koda yaushe zaka same shi da carbi a hannun sa yana yiwa mahaifiyarsa addu'a  kuma kullum sai ya zubar da hawayen rashinta domin suna kaunar juna sosai bashi da wanda ya fiyemasa Ummansa a duniyan nan.

*WAI WACECE KADDARAR ABDUL-ALI KUMA MIYE MIYE DALILIN DA YASA YAKE KIRANTA DA KADDARAR SA🤦🏻‍♀? WAI KODAI BATA DA SUNA NE😲.....OHO😏MU CIGABA DA BIBIYAR ABDUL DON SANIN KADDARAR SA🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀*



*LAGOS*

Bintu tana zama gidan uncle dinta anan Lagos taji dadin zama dasu domin suna debe mata kewar gida sedai ta kasa daina tuna damuwarta kullum tana cikin addu'a Allah ya sada ta da farincikin rayuwar ta,wataran idan suna zaune da Nabila hirarsa kawai take masa har Nabil ma da yake namiji indai suna tare saita bashi labarin farincikin ta.




*🕯Halieymerh Ameen🕯*

Comments

Popular posts from this blog

ANCUCI HIJJABI BY FAYEEEEEEX M USMAN

ANCUCI🤦🏼‍♀HIJJABI _*TRUE*    *LIFE*   *STORY*_ ✏ _Writen by_ *fayeeeeex m usman* 💦💦 *Talented writers forum*  💦💦 *had'in kanmu abin alfaharinmu🤝kungiya d'aya tamkar da dubu* _domin samun littattafan mu shiga.... _To get access to talented novels check_ http://talentedwrittersnovel.blogspot.com/ 💚💙❤✨             💃🏼💃🏼💃🏼✨ 🍭🍡🥂✨ 💙💚❤ *zuri'a d'aya soyayyama guda d'ay~a karda kutam bay~a rabu da* _jun~abana mun~e wannanba❤y'an uwan jun~a soyayy_ *a had'uwar jin~i soyayyar zuciya ba ayimata magani💙wannan pg d'in nakune ku kad'ai my* _lovely family bani da kamarku har abada kuneni inbaku ni bakomai bace soyayyata agareku d'orarriyace tarihina daku_ *dauwamammeni bazaku ta6a i...

NADAMAR SOYAYYA

💞 *Nadamar Soyayya*💞 ( a true life story) 🖊by *_Reefat Yahya_*💞 *BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM note dat wannan labarin ya faru ne da gaske ba kirkirarsa nayi ba , Allah yasa muyi aiki da darusan dake ciki musamman 'yan matan yanxu kuma wannan shine labari na farko da na rubuta based on true life story Allah ya bani ikon gamawa lafiya ameen* 👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 *Baiwar Allah*: _Salam sister Reefat ya kike ya fama da jama'a_ *Reefat* _lafiya Alhamdllh sis ya kike_ *Baiwar Allah* _lafiya sai godiya, don Allah tarihin rayuwata nake son na baki Ki rubuta_ *Reefat* _OK ba damuwa Allah yasa mu dace_ *Baiwar Allah* _ameen nagode sosai amma don Allah Ki boye sunana da sunan garin mu , ina son labarina ya zamto darasi ga sauran al'umma_ *Reefat* _ba komai insha Allah, Allah ya shige mana gaba_ *Baiwar Allah* _ameen nagode sosai da karamci_ *Kada...

Nadamar soyayya

💞 *Nadamar Soyayya*💞 ( a true life story) 🖊by *_Reefat Yahya_*💞 💦 *Talented writers forum*  💦 *had'in kanmu abin alfaharinmu🤝kungiya d'aya tamkar da dubu* _domin samun littattafan mu shiga...👇🏻👇🏻👇🏻 _To get access to talented novels check_👇🏻👇🏻👇🏻 http://talentedwrittersnovel.blogspot.com _dedicated to *Zaleefah S Nalado*_my kwalliyas😘😘 *5&6* Da gudu khairat ta shiga dakin har sai da tasa ummi ta tsorata tayi tunanin ko wani abun ne ya faru.. "Khairat lafiya kike gudu haka?" Ummi tace cike da fargaba. "Bakomai wallahi ummi sai alkhairi" khairat ta ba ummi amsa cikin fara'a. "Toh alhamdulillahi wlh har hankalina ya tashi na dauka wani abun ne ya faru kike irin wannan gudun haka kuma wai kha...