💧💧💧 *FEENERT* 💧💧💧
{ ~*Diyar sarki ce*~}
*Talented writers forum*
*(T. W. F)*
*By*
*pherteenjeey*
*Dedicated to Islah tee (Mrs. Jameel)*
*Gaisuwa ta musamman ga*
*Zarah Ms writer din juyin lamari*
*Maman Fareeda writer din Dan Maliki mai hadarin naira inayi miki fatan alkairi da kammala shi ubangiji ya bada ikon cigaba da (samun wuri) lafiya ILYSVM* 💕
❤❤❤❤❤❤
02
Rarrashin baba ya farayi amma fur taki yadda da shi dole saiya fitar da yarinyar, haka ya fita ya koma dakin zulai ya qirga mata yadda sukai da baba kuka ta dinga yi wiwi hadda majina, hakuri yake bata da kyar tayi shiru yace daina kuka yanxu zan je na fadawa Malam habu idan yaso yazo yayi mata nasiha ko taji
Toh zulai tace ta dauki jaririyar ta Goya ta a baya shi kuma Malam iro ya koma gurin Malam habu da Isar sa ya iske bayanan, ya tambayi mutanen gurin suka fada masa ya shiga gida.
Yaro ya aika yayi sallama dashi yana fitowa yayi masa bayanin yadda sukai da baba, hakuri ya qara bashi sannan yace suje ko zai jarraba tashi nasihar,,,
Suna isa gida suka shige sashen baba tana ganin Malam habu ta washe baki tayi masa sannu da zuwa amsawa yayi rai a sake tayi mai iso har rumfa sannan ta kawo masa ruwa yasha.
Gaisawa sukai sannan Malam habu ya fara koro mata bayani, kamar haka, kamar yadda kika ganni a gidannan baba kinsan alfarma nazo nema a gurinki Dan Allah baba kibar iro ya rike wannan jaririya, kai Malam habu dakata oho zuwa yayi ya fada maka qarya da gaskiya to wannan shegiyar yarinyar ba'a gidannan ba wallhi, haba baba taya za'ai kice mata shegiya bayan ba'a San iyayen taba Malam habu ne yake magan cikeda damuwa a fuskar sa, yooo Malam habu inba shegiya ba wadansu iyayene zasu haifi yayrinya su ajjeta a bola, Aah ba haka bane baba kowa da qaddararsa a rayuwar sa, inajin sato yarinyar akayi aka jefar Dan Allah baba kiyi hakuri kibar yarinyar nan takai shekara goma sha biyar a lokacin tayi wayo inya so sai ta nemi iyayen ta da kanta, da kyar da sidin goshi baba ta yadda, shidai Malam iro yana tsakar gida yana jinsu, godiya Malam habu yayi yasa hannu a aljihu ya fito da Dari biyar ya bata, tana washe hakora ta karba tayi godiya sannan tace dashi ya gaida gida, fitowa yayi suka wuce cikin gida gurin iyalan sa suna shiga larai ta fara bala'i da zage2 to Su Oo ko me ya kawosu aka bibiya anzo munafurcin da aka saba ne ko kulata basuyi ba suka shiga dakin zulai.
Gaisawa sukai Malam habu ya karbi jaririyar yayi mata addu'o'i sannan yace da Malam iro wani suna kuka saka mata.
Sai a sannan suka tuna basuyi mata suna ba, zulai ce ta sunkuyar da kai tace ina Neman wata alfarma Malam a gurinka, wata irin alfarma ce zulaiha fadamin kowacce iri ce indai batafi qarfina ba zanyi miki ita, godiya tayi sannan tace dama sonake asaka mata sunan mahaifiyata.
Farin cikine ya cikasu Su duka Malam habu da iro sai shi mata albarka sukeyi a take a gurin Malam habu yayi mata huduba da sunan mahaifiyar zulai wato *NAFISA*.
Tun daga wannan lokacin rigima take hawa a gidan Malam iro zulai bata da ikon fitowa tsakar gida sai Malam iro yana gida, larai kuwa da yayanta kullum suna qudure da niyyar dauke yarinyar su jefar da ita.
A haka rayuwa taci gaba da gudana a gidan Malam iro dadi da badadi .
Kuma ayau ne Nafisatu tacika shekara hudu cif da haihuwa inda Malam iro ya sanyata a makarantar allon Malam habu, kullum Malam iro ne zai kaita ya dauko ta saboda masifar larai.
*Shin wanene Malam iro*
Malam tukur yana da mata daya mai suna Halima (baba) wadda ta kasance bata haihuwa ga masifa da San abin duniya arashin haihuwar ta ya qaro aure inda ya auri kanwar abokinsa wato maryama, ta kasance mai addini da tarbiyya, Watan maryam uku ciki ya bayyana zo kaga murna gurin ta da mijinta, tun daga lokacin Malam tukur yake bata kulawa ta musamman a dalilin haka ne Halima ta tsani Maryam, haka suka cigaba da rayuwa dadi da rashin sa inda cikin maryam ya tsufa haihuwa yau ko gobe.
Wata ranar alhamis maryam ta Tashi da naquda cikin ikon Allah ta sauka lfy inda ta haifi santalelen yaronta namiji.
Da labari ya iske halima Maryam ta haifi da namiji kamar ta hadiyi zuciya ta mutu, tun daga wannan rana halima ta tsani maryam da danta, a kwana a tashi babu wuya gurin Allah yau ne sunan maryam inda yaro yaci suna Ibrahim, amma suna kiransa da iro.
Ahaka rayuwa tacigaba da tafiya inda yau Malam tukur ya tashi da shirin tafiya birni domin sayar da wani kaso a dukiyar sa domin yayiwa dansa karatu.
Shiri yakeyi domin ya kusa makara, sallama yayi da iyalansa ya Kama hanya ya fita, tunda ya fita maryam gaban ta yake faduwa.
bangaren malam tukur kuwa yana fita ya wuce gidan abokinsa dama tare zasu tafi da isarsa ya iske shi a kofar gida dama shi yake jira, bashi hannu yayi suka gaisa sanna suka kama hanya zuwa tasha.
Suna Isa suka iske saura mutum uku motar ta cika babu musu suka shiga, sannan suka jira dayan yaxo suka tashi, tafiya sukeyi cikin nutsuwa, tafiya sukeyi babu qaqqautawa sunje dai2 wani junction sai ga wata qatuwar mota ta bigi tasu motar.
Bugar ta keda wuya motar ta kifa ta dinga juyi har saida ta shiga wani daji. babu shiri aka kira ambulance aka ciro wadanda suka mutu wanda suka ji ciwo aka tafi dasu asibiti gaba dayan Su.
*Shin Malam tukur da abokinsa mutuwa sukayi ko rauni sukayi sai kun biyoni zakuji cigaban labarin*
Pherteenjeey✍🏻
fatimaauwal1999@gmail.com
09077726072
4 comment only👌🏻
💧💧💧 *FEENERT* 💧💧💧
{ ~*Diyar sarki ce*~}
© *Talented writers forum*
*(T. W. F)*
*By*
® *pherteenjeey*
*Dedicated to Islah tee (Mrs. Jameel)*
*Gaisuwa ta musamman ga*
*Dahara Nuri Galadima namcy na inayi miki barka da dawowa da fatan kin dawo 9ja lafiya tnx 4 your support n care luv u lodi lodi Namcy muahh*💋💋💋
03
Ana isa asibiti aka wuce dasu emergency aka basu taimakon farko. Aka ware matattu aka sakasu a mutuware, Allah sarki duniya sai dai muce Allah ya jiqan wadanda muka rasa ciki kuwa hadda Malam tukur, duniya kenan. acan bangaren masu rauni na hango abokin Malam tukur nace dama shi bai mutuba, ikon Allah kenan, kwanan sa daya yace a sallame shi domin akwai Dan uwansa a cikin matattu Dan.haka zaije ya kai gawarsa Gida a sallace shi.
Babu bata lokaci aka sallameshi yayi duk wani abu daya kamata yayi ya wuce da gawar abokinsa garunsu.
Acan bangaren iyalan Malam tukur kuwa maryam da danta sun damu sosae inda halima kuwa ko ajikinta, dan har gidan abokin malam tukur taje akace mata basu dawoba, Ai kuwa tana shirin fita domin takoma gidan abokin mijinta tayi kicibus da shi a cikin gida tare da wasu mutane.
Ahhh sannun ku da zuwa maryam ce take magana cikeda damuwa a fuskar ta, yawwa maryama ya gida, cewar abokin mijin nata.
Yawwa ina uwargidan taki take ne??? Hmmm sai dai a duba dakinna ta ko tana nan. Yawwa to duba ki gani ko tana nan, juyawar da zatayi sai gata nan ta taho.
Nasiha yayi musu mai ratsa zuciya inda ya basu hakuri sosae akan duk abinda ya sameka, sannan daga bisani ya fada musu cewar mijinsu ya rasu da abinda ya faru da Su.
Tun kafin ya gama maryam ta zube a gurin ta dinga kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro.
Da kyar aka bata hakuri tayi shiru, halima kuwa cewa tayi a ranta shikenan yanzu zanyi yadda nakeso a gidannan Dan wallahi sai zaman gidannan ya gagareki ke da danki.
A fili kuwa kuka take hadda majina tana cewa shikenan gatana ya qare Malam ya tafi ya barni.
Hakuri aka bata tayi shiru sannan aka yiwa Malam tukur sutura aka kaishi makwancin sa Allah sarki duniya.
Tun daga wannan rana Halima ta takurawa Maryam da danta batada sukuni ko kadan inba abokin mlm tukur ne yazo ba, shi kadai ne yake taka mata burki takeji.
abincin da zasuci ma gagarar su yakeyi inba shine ya Kawo ba.
Ahaka rayuwa taci gaba da tafiya a gidan Malam tukur inda a halin yanxu iro yanada shekara 27 maryam kuwa kullum babu lafiya iro ya rasa yadda zayyi ga babu abinci ga rashin kudi ballan tana ya kaita asibiti.
Yau ta Kama ranar lahadi cikin dare maryam ta dinga aman jini ba qaqqautawa kafin gari ya waye Allah ya karbi abinsa.
Wayyo Allah maraici (littafin zeenasir) shikenan iro ba uwa ba uba sai dai muce Allah ya jikan Maryam yakai rahama kabarin ta.
Da safe kuwa aka shirya ta aka kaita makwancin ta, iro yasha kuka kamar karamin yaro.
Halima kuwa murna ce cike a ranta yanzu burinta ya fara cika saura iro shima ya mutu ta gaje dukiyar gaba daya, *(Dama kafin Malam tukur ya mutu ya hada kaf dukiyar sa ya bawa Maryam sai wadda tayi saura a gurin abokinsa)* da wannan farin ciki Halima ta kwana a ranar, bayan mutuwar maryam da kwana arba'in abokin Malam tukur yazo da mai gari da alqali aka raba dukiya, inda iro ya samu kaso mai tsoka.
Halima kuwa kamar ta hadiyi zuciya ta mutu Dan bakin ciki.
Tun daga wannan rana halima (baba) take tarairayar iro kamar danta data haifa.
Samun iro tayi a dakinsa yanata tunani da sallama ta shiga, kai iro meyasa meka kake kuka, laa babu komai baba me kika gani, hawaye na gani yana yawo a idonka.
kadai na kuka haka sannan ka cire damuwa zuwa nayi da wata magana mai mahimmanci a gareka, to baba inajin ki cewar iro dayake gyara zaman sa.
Da zaman da kakeyi iro kayi aure mana jiyar maganar ta doki kunnen sa, toh ni baba wacece zata soni bayan ba gurin kowa nake zuwa ba.
hamdala baba tayi aranta tace faduwa taxo dai2 da zama a fili kuwa haka tace karka damu akwai yar qanwata na yaba da hankalinta sunan ta larai itama bata kula kowa cewar baba.
Iro dai shiru yayi domin baisan mezaice mata ba harga Allah shi baya zuwa gurin wata budurwa sannan kuma bazai iya bijirewa maganarta ba.
Dago kansa yayi yace babu komai baba na amince da maganarki kije kiyi duk abinda ya dace ayi. zo kuga murna gurin baba burinta ya cika
Fatimaauwal1999@gmail.com
Pherteenjeey✍🏻
💧💧💧 *FEENERT* 💧💧💧
{ ~*Diyar sarki ce*~}
*Talented writers forum*
*(T. W. F)*
*By*
*pherteenjeey*
*Dedicated to Islah tee (Mrs. Jameel)*
04
Albarka ta dinga shi masa tace dashi bikin bazai wuce nan da wata 1 ba, ba komai iro yace ya koma ya kwanta.
Baba kuma ta fita daga dakin domin ta kimtsa taje ta sanar da qanwar tata, tana isa gidan ta zayyane mata komai murna ce ta cikata. Ta dinga yiwa yayar tata godiya.
Rana bata qarya sai dai uwar diya taji kunya, a yaune ake daura auren larai er qanwar baba da iro Dan kishiyar ta. Bakin baba kamar ya yage don murna saboda burinta ya kusa cika.
Da daddare aka shirya amarya larai aka kaita gidan mijinta, inda acikin gidan ya gyara wani guri inda zai zauna da iyalansa.
Tun bayan Biki da sati uku larai ta fara nunawa iro ainihin halayen ta, ko sau daya baba bata taba yiwa larai fada ba.
Idan ma iro yakai qarar ta sai baba ta daura laifi akansa tun daga lokacin ya daina gaya mata komai Nasa.
Ahaka larai ta sami ciki har ta haifi danta namiji sak kamarsu daya da ita.inda yaro yaci suna sule.
Bayan shekara uku ta kuma haifar diya mace mai suna mejidda, sai kuma bayan shekara daya da wata Tara ta haifi yarinyar ta mai suna lami.
kaf dukiyar iro larai ta kwashe ta bawa baba ita, a dalilin haka iro ya dawo matsiyaci ( da yai magana cewar baiga dukiyarsa ba sai sukace ai daya fitane barayi sukazo suka kwace komai na gidan haka ya dau hakuri).
Tun daga lokacin baba ta sauyawa iro fuska masifar yau daban ta gobe daban.
Haka ake rayuwa gidan malam iro cikin qunci sai ya fita yayi ciyayi ya sayar sannan ya samu ya bawa larai tayi cefane.
Randa kuwa ba'a samu ba sam babu zaman lafiya a gidan.
Tunda iro yaga tsantsar Halin baba da larai shine ya samu wata yarinya mai hankali a layinsu ya aura wato zulai, shekara zulai daya a gdn larai ta haifi er ta inda tasaka mata sunan baba wato Halima, (tunda zulai tazo gidan bata taba samun kwanciyar hankali ba larai da yaran ta suyi mata baba ma tayi mata, sai malam iro yazo take samun kwanciyar hankali).
*cigaban labarin*
A haka rayuwa tacigaba da gudana a gidan malam iro, inda yanxu nafisat (feenert) take maida hankali a karatun ta, Dan takusa hadda ce izu goma, bangaren boko kuwa yanzu tana aji biu saboda qwazon ta.
Zulai kuwa gwargwadon iko tana farantawa yarinyar tata rai, duk abinda takeso tana bata.
Wata rana feenert ta fita tsakar gida yin wanke2 sai ga lami ta fito daga bayan gida, wani wawan mari ta dauketa dashi ke shegiya uban waye yace ki taba mana kayan en halal lami ce take magan ciketa facin rai afuskar ta.
Da gudu feenert ta koma daki domin taji marin har cikin ranta.
Tana shiga ta fada kan cinyar innar ta kuka take wiwi kamar ranta zai fita inna (zulai) ce take tambayar ta ke mamana ke dawa tana sheshsheqa ta fada mata inna ba lami bace ta nareni wai karna qara taba kayan en halal wai ni shegiya ce.
Daina kuka mamana keba shegiya bace ba domin nice na haifeki malam kuma shine baban ki yawwa inna ta daman nasan lami ba gsky ta fada ba rungume ta innar ta tayi aranta kuwa cewa tayi oh ni naga ta kaina ace wannan qanqanuwar yarinyar lami take cewa shegiya meta sani.
Allah ya kyauta juyowar da zatayi taga feenert har tayi bacci, kwantar da ita tayi ta fita tsakar gida domin qarasa wanke2.
fitarta keda wuya ta cigaba da wanke2, sallama taji ana dokawa ta amsa shigowar da za'ayi tayi tozali da fuskar larai wata uwar harara ta doka mata sai da tazo dai2 da ita ta fara yada mata da bakaken maganganu mejidda ce ta fito daga uwar daka domin jin hayaniyar da akeyi a tsakar, fitowar ta keda wuya ta amshe da....yo ce mama ai idan aka bibiya itama shegiyar ce bata rufe baki ba taji wa2n mari a fuskar kafin ta dago taji an qarayi mata wani hagu da dama. Dagowa tayi da zummar ganin waye ya mareta sai taga ....wa babanta wallahi kika qara zagin matata sai nayi miki dukan da babu wanda ya taba yi miki shi.
kai malam akan wannan shegiyar matar taka ka dakar min ya wallahi yau sai anyi ta a gidannan.
Wucewa tayi fuuuu sai a bangaren baba taja burki, kwashe labari tayi ta fadawa baba ai kuwa kamar ana tsungurar ta tace muje naci ubansu su duka fita sukayi tsakar gida amma me sai sukaga babu kowa a gurin.
Mejidda ce tace da larai kina barin gurin nan suka shige daki suka kulle.
ashar suka dinga yi, sannan daga bisani da sukaga sun gaji shine kowa ya tafi dakin sa.
Akwana a tashi babu wuya gurin Allah feenert ta sauke Alqur'ani sannan tasan littafai da dama a bangaren hadda kuwa tana da izu arba'in da biyar, a boko kuwa tana ajin qarshe na qaramar sakandare wato jss 3, kyawun ta sai fitowa yakeyi inda a yanxu feenert tana da shekara goma sha biyar. Kuma a yaune baba ta bujuro da alqawarin da sukai lokacin da aka kawo feenert gidan inda ta fito tsakar gida tana ta banbami, ita ala dole sai feenert ta bar gidan a yau ba gobe ba.
Wannan magana ta tayar wa zulai da malam iro hankali ba qaramin kidime wa sukai ba. da kyar ya bata hakuri cewa ta bari zuwa wani lokaci. Sallamar feenert ce ta ankarar da su juyowa sukai gaba daya suna kallan ta domin wani farin ciki ne dauke a fuskar ta, wani tsawa larai ta daka mata ke shegiya garama kidaina wannan farin cikin da Kikeyi domin kuwa kin kusa barin gidannan, ko kulasu batayi ba ta shige daki domin inda sabo ta saba jin wannan bakaken kalaman daga bakin su.
fatimaauwal1999@gmail.com
Pherteenjeey✍🏻
Comments
Post a Comment