💦💦 HAJJA HADIZA💦💦
🔥🔥🔥🔥🔥
A true life story with ultimate fire roaming in circles
🔥🔥🔥🔥🔥
💦Talented Writers Forum💦
TWF
Hadin kanmu abun alfaharin mu🤝🏻
kugiya daya tamkar dubu👌🏼
http://talentedwrittersnovel.blogspot.com/
Written & story by Qz
My greetings to Yar Aljanna(namesyy) on the death of her grandpa,may Allah grant you & ur family the hrt to bear d lost & may jannatul firdaus be his final abode😪
💦21-25
Washe gari da safe takira wayarsa taji akashe,haka tayita kira har yamma amma baya zuwa duk dai zance dayace wai swtchoff,karshe dai bayan sallar magrib ta kira Hajja Ghaji akan tazo ta rakata gurin saurayin yayanta ko zata samu information akan inda zata sameshi.
6angaren Saleh kuwa hankali kwance har yama manta dacewa wata ta kirashi jiya harta 6ata mishi rai don kuwa tunda yatashi ya cire sim din data kira dashi yasa wani a cikin wayar yaji damuwarsa ta tafi.
Ranar ma a unguwar su Hafsa budurwarsa ya yini daganan yadan zaga gun majalisa aka ta6a hira kafin ya dawo gida.
Meanwhile a 6angaren su Hajja Hadiza har sun tari dan adaidaita don shigowa anguwarsu Sule,sunkoyi dace domin suna sauka suka hango shi a bakin masallaci, batare da tunanin komi ba suka karasa inda yake cike da jindadin ganinsa, shi kuwa mamakine ya kamashi akan meya kawosu a wannan lokaci kusan ishai, ganin cewa gunsa suka nufo yasa ya tashi yaje yasamesu.
"Hadiza lafiya na ganki a wannan lokacin kusan goshin ishai?"ya tambaya yana nazarinta
"Lafiya ba lafiyaba yaya, dama munzo ne akan kozaka nuna mana gidansu abokinka!" ta fada kai tsaye
"Abokina kuma, wanne toh a ciki, ince dai bawani abun ne yafaruba?" yana magana yana tunani kala kala
Hajja Ghaji tayi saurin cewa"eh toh abokinka wanda kabamu lambarsa jiya dakazo dama munkira shi yau ne wayar akashe tun safe kuma munada wani muhinmin business dashi shiyasa muke nemansa".
"Au okay wai Saleh kuke nufi,inaga kila yacire layin awayarsa amma barin baku sauran layikansa guda biyu,amma samun shi a gida yanzu zaiyi wuya kila ma yana majalisa ta chan gangaren babban masallaci". yafada yana lalibo numbern
yana gama fada musu sukayi mishi godiya suka kama hanyar majalisan da ya kwatanta musu,shikuma ya fadane batare da tunanin ko zasu iya zuwa ba.
bayan sunwuce ya tsaya tunanin hali irin na yaran zamani toh koma wani irin abunw ai sai subari zuwa gobe tunda bagun mace yar uwarsu bane, gashi sai wani rawar kafa Hadiza keyi "Allah dai yasa bawata akasa". yafada tare da komawa bakin masallacin
Su kuma anasu 6angaren har wajen majalisan sukaje, ai kuwa sunyi saa yana gurin,dialing dayan layin da akabasu sukayi ai kuwa bajimawa yashiga amma dai baa dauka ba saida sukayi kira sau kusan uku ana hudun ya dauka.
"Hello waye ne naga anata kirana lafiya koh?" ya tambaya cikin jin haushinsu domin ya hango su kuma yagane Hadizan saboda kasancewa inda suka tsaya akwai haske sau dai basosai ake ganin fuskarta su ba.
"Lafiya kalau, dan Allah ko zamu iya ganinka minti biyu,muna daga gefen inda kuke zaune". tafada cikin lumana
Sai da yadan jinkirta kadan kafin yace "okay gani nan zuwa".
Kashe wayar tayi murna fal ranta "kawata kinga wai yana zuwa fa".
"Amma dai wallahi yacika dan rainin wayo sai da ma tayu tubani kafin ya amsa da zaizo din mtsss". ta fada cikin jin haushinsa
Hadiza ce tayi charaf tace "A'a kar ma kifara ai banta min shi ehe ni duk abunda zaiyu bazai dameni ba indai zai na kulani".
Tana gama rufe bakinta sai gashi ya iso yana wani yamutsa fuska kamar yaga kashi itadai Hajja Hadiza bata ji haushi ba amma Hajja Ghaji kam kamar ta rufeshi da duka aranta tace "dan rainin wayo wato ma irin ga matsiyata nan sunzo nemansa mtss".
Sannu Sale yanzu muka hadu da Sule abokinka ya bamu numbrnka,nayita kiran dayan layin naka baya shiga dama shine mukazi muji ko lafiya dai koh". tafada ba ko kunya
Shikam abun ma mamaki ya koma bashi lailai kuwa wannan yarinyar da alama dai bahuwace babba ma kuwz ya fada a ransa kafin yace "eh lafiya kawzi banason yawan yin wayar ne shiyasa
na kashe don kar adameni dayawa kinsan wasu matar ba hankaline dasu ba sai surin ga kai kansu inda baasan suna yiba ma". yafada cikin gatse yana murmushin mugunta
Batare da takawo komai aranta ba tace "eh wallahi a wasu matan basuda kunya gaskiya,toh tunda kana lafiya mu zamu koma gida amma zankiraka anjima, wannan kawatace Hajja Ghaji". tafada tana nuna masa Ghaji wacce mamakin maganar da ya ya6a musu kadai ya cika zuciyarta ga karin abun haushin ma wato ita hadizan bata fahimci hausar ba harda tayashi zagin..
😍DEDICATED TO S.U❤
✨QUEEN ZAHRA✨✍
Comments
Post a Comment