✈✈✈JIRGIN SO✈✈
🎯8🎯
💦TALANTED WRITERS FORUM💦
NA RUKAYYAT CE
washe gari tun 7 suka tashi suka kara kimtsa kayansu sukaje kukayi ma yen gidan sallama suka neme driver yakai su gidan su zee.
suna hanyane zee ta kira su
'hello aysha kun kamo hanya ko'
'eh mun kusan zuwa'
'toh sai kunzo' inji zee
sallama sukayi sannan bayan about some minutes suka isa gidan su zee.
bakin gate aka ajesu suka shiga ciki.
suna shiga suka tadda maman su zee a parlour din gidan ita da zee da masu aiki 2 suna saka kaya cikin jaka wato wanda zaa raba a gun.
sallama mukayi suka ansa
kallon mu maman su zee tayi tce "har kun zo amma kam kun yi sauri."
"hmm eh wlh mama kinsan driver din namu da mugun gudu yake. "
"hkane "maman zee ta fda "tunda kun karaso ku zo ku taya su bari in je in yi wanka banyi ba kafin su alhaji su sauka dan sunce min by 9 jirgin zai sauka"
kallon zee nayi wanda ta hakirkire tana ta aiki
dariya nayi nace "su zee bbu magana ne abun"
harara na tayi tace" hmm ke dai zo ki sa hannu wlh bayna ke ciwo "
zuwa mukayi ni da murja muka taya su bayan mun gama ne gurin 8 muka shiga dakin zee wanda ya kawatu da purple colour.
wanka zee tayi sannan tasa atampha dinta wnda muma atampha mukasa sannan muka sauko kasa dan mu ci abincin safe.
muna nan zaune maman su zee ta sauko cikin kwalliyanta a zuciyata nace kai maman su zee ta iya kwalliya gata matar da kyau ba kadan ba. maman su zeene tace' zee kin fada ma adamu yenzu yakamata yaje ya dauko su alhaji kuwa' (adamu driver din su zee ne) 'ehh yama tafi dan naji fitar motar' tou maman su zee ta fada sannan ta koma cikin parlour din taxauna tan kallo. munazaune muna hira gurim karfe 10 muk ga an bude kofa baban su zee ne ya shigo mamaki mukaji da bamu ji shigowan mota ba.
da driver biye dashi da akwatina
dga byan shi kuma yaya saeed ne wanda ninaga ya kara fari akanda da kyau kuma kai yaya saeed gskya mai kyau ne yna kma da mamanshi sosai kuma ko da yke miskili yna da nashi kyan .
duk acikim second uku nayi tunanin nan
tashi mukayi muka karasa bakin kofan
'Ah dan ummi ya dawo oyoyo oyoyo kaga kuwa yarda ka chanxa'' cewar maman zee tana rungume ya saeed.
murmushi shima yayi yana rungume ta'' ummi I miss u too much kullin sai nayi magafarkin gida''
''ina wuni yaya''cewar zee kenan .''lfy lau'' zainab autan ummi ya gida ya karatu dayake kingama secondary ko''
''ehh zainab tace na gama yaya''
'' toh alhamdullilah'' yace mata
ni dake bayan ummi ne na da fito tare da gaida shi
'' lfy lau ah badai aysha bce ta girmahka'''
maman zainab tce'' ai tsawo gare ta''
murmushi yaya'' ya kike aysha ya gida ina yayyanki da almu duk suna lfy ko''
'' lfy lau suke yaya''
baban su zainab ne yayi gyran murya tare da cewa' ''toh anga dan momi an manta da daddy.''
maman zee tace''kai ko kasan cewa yarda muka dade bamu ganshi ba ai dole mu manta dakai tafada tana murmushi''
''lallai kam aysha ya babanki''
''lfy lau baba ina wuni''
''lfy lau aysha''
bayan mun gama gaisawa ne da nuna farinciki suka kara sa dakinsu da baban zee da ya saeed dan suyi wanka su ci abin ci
Comments
Post a Comment