*Whatsapp no*
08109990994
[9/29, 9:06 PM] Ma Asaa4😘: *10/8/2017*
*3:00am*
'" *ZAFIN KISHI* '"
*WRITED BY*
*husnah mb*
*EDITED BY*
*TEEMAH JALO*
*31.*
Kwanaki nata tafiya yau Satin manal guda a gidan Aliyu yau zai koma dakin khadija, misalin karfe 9 na dare suna zaune kan kujera suna kallo cikin jikinshi ta nade kaman wata mage yanajin dadi yadda manal take tarairayarsa kaman wani jariri abun na matukar faranta masa agogon hannunsa ya kalla yaga har fast 9. A kunne ya rada matamy Queen i have to go dago kai tayi tana murmushi zan koma dakin khadija kinga har fast 9 kartace munshiga hakkinta, murmushi tayi a ranta tanajin dadi Allah ya bata miji na gari me hakuri da sanin yakamata...
Tashi yayi plz _my Queen_ _take care of ur_ _self for me_
Murmushi tayi ta lumshe idona hakan yana matukar burge Aliyu musamman ma idqn ta juya idon tannan manya manya sai yaji har cikin ranshi.
''I _will gonna miss u my_ Queen
'' _miss u more habibi_
Jikinshi babu kwari ya fita shi kanshi yasan babu shakka xaiyi missing din lallausan jikin Queen dinshi...
Abunda ya dade bai gani ba yau ya tarar gun khadija tayi girki tana zaune tana jiranshi, dago kai ta sake masa wani murmushi murmushin shima ya mayar mata..
abincin data girka sukaci shidai Aliyu kawai yaci ne kartace ta masa girki baici ba amma bawai dan abincin yayi dadi ba hasali ma daker yake tura abinci, sunan wani abu wai ci karka mutu😜
Around 9 o'clock Aliyu ya tashi daga bacci wanka yayi ya fito yana neman khadija dubawa yayi bai
ganta ba saiyayi tunanin ko tana kitchen ne, downstairs ya sauka saiya sameta zaune a falonsa na kasa tana kallo gaisheshi tayi yace mata kijiran anan ina zuwa dakin manal ya nufa zaune ya sameta gaban mirrow alaman wanka tayi tana kwalliya..
''Morning habibi
morning how are u my Queen' am fyn tace tare da sakar masa wani murmushi
"My Queen 'yes habibi what happen kizo ki sameni falo kasa inason yin magana daku keda khadija 'Ok tace ta nufi bakin wadrop tana neman gele....
Gele ta dauko ta biyoshi a bayah zaune ta samu khadija kan One seater ta dqura daya kan daya da remote a hannunta zama tayi kusa da kujeran da Aliyu ya zauna manal ne ta fara dagawa khadija gaisuwa sannan ta Amsa amma hankalinta yana kan tv....
Shiru sukayi babu wanda yacewa kowa uffan bayan gaisawan da sukayi
Aliyu ne yayi gyaran murya ya fara da cewa dama Abunda yasa na tara ku anan ba wani abu bane inaso na sanar muku ne zan raba kwana
kaman yadda Allah ya umarcemu da in munada mace da yafi daya muyi hakan, don haka kwana 2 biyu zannayi a dakin ko waccen ku sannan daga yau dinnan da nake magana na daina bin kowa dakinta dakina zakuna zuwa, na 2 kenam na uku kuma inaso in nemi shawaranku ne akan maganan girki zakunayi tare ne ko kuma ko wacce xatayi nata wanne kukaga yafi muku ai kafin ya rufe baki ma khadija ta karbi maganan...
A gsky babu wani maganan kowa tayi nata kawai anayi a tare ni inaga kaman yafi ita dai manal batace komai bah tana jinsu shiru yayi baice komai ba sanda ya bari khadija tayi shiru sannan yace To ke yanxu manal hakan ya miki ko kuma kinada wata magana babu tace kanta
a sunkuye tana kallon kasa duk da bataji dadin hada girkin ba ita indai zabi za,a bata da cewa zatayi kowa yayi nashi amma tunda tace haka bata barta a hakan yanxu intayi magana Aliyu xaiyi tunanin tana neman fada ne, hakan yayi miki Aliyu ya kara tambayan Manal tace yayi yace to shikenam babu matsala zaki iya tafi.
Tashi tayi ta haura uppstairs.....
Muje zuwa.........😉
*Whatsapp no*
08109990994
Comments
Post a Comment